Posts

Shatiman ABU Zaria

Image
An naɗa Daud Uthman Babangida a matsayin sabon Shatiman jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria a lokacin gudanar da shagulgula da kuma baje kolin al'adu daban-daban a faɗin najeriya na shekarar 2023. Shatiman ABU 2023. Taron baje kolin al'adun na wannan shekara wanda ƙungiyar dalibban jami'ar suka shirya ana yi masa take da ABUCultural Carnival 2023, ya samu halattar dalibbai a ko wace tsangaya da rassa na faɗin makarantar. Shatiman ABU 2023. A wurin an naɗa Daud Uthman Babangida a matsayin sabon Shatiman ABU. Shatiman ABU 2023. An haifi Daud Uthman Babangida a ranar 28 ga Watan Oktoba 1995 a karamar hukumar Chikun ta Jihar Kaduna dake arewacin Nigeria. Daud ya girma a jihar Lagos dake kudancin Nigeria, inda ya yi karatun firamare da sakandare duka a makarantar Taoheed international school dake Lagos. Shatiman ABU 2023. Daud ya kammala karatun diploma daga kuma yanzu haka yana matakin karshe na digiri ɗinsa na farko a sashin karatun aikin jarida na jami'ar Ahmadu Bello dak...

Yadda aka gudanar da baje kolin al'adu a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria.

Image
Yadda dalibban jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria suke murna tare da gudanar da wasa a na baje kulin al'adu na wannan shekara ta 2023. Ana gudanar da irin wannan baje kulin al'adu a duk shekara, idan ake da sarkin ABU da kuma sauran sarautu da suka haɗa da shatiman Abu, makamam Abu, sarauniyar Abu da dai sauransu . ku kalli yadda abubuwan suke a cikin waɗannan zafafan hotona.

Cristiano Ronaldo.

Image

Matashiya Yar'shekaru 28 Ta Zama Minista a Nijar.

Image
Gwamnatin soji a Nijar sun Naɗa matashiya mai suna Guichen Aghaichata ATTA, Yar'shekaru 28, a matsayin sabuwar ministar yawon bude ido da kasuwanci ta kasar. Wannan naɗi na zuwa ne bayan hambarar da shugaba Bazun a watan jiya. Haryanzu ƙungiyar ECOWAS na adawa da juyin mulki da sojojin kasar Nijar suka yi. Ita dai matashiya Aghaichata mace ce mai himma sosai wajen inganta dabi'un, al'adu da kuma kokari don kawo cigaba ga matasa.  Ta yi karatu idan da ta yi da digiri biyu a fannin kasuwanci a kasar Maroko. Bashar Muhammad.

Yaƙi da Juyin Mulki ko Yaƙi da Yan'ta'adda?

Image
Yayin da wa'adin mako ɗaya da ƙungiyar ECOWAS ta bai wa sojojin da suka yi juyin mulki a kasar Nijar su mayar da mulki ga hamɓararren shugaban ƙasar Mohamed Bazoum ya cika a ranar Lahadi, tana kasa tana dabo saboda duka ɓangarorin biyu na tsaka mai wuya wajen ɗaukar mataki na gaba kan wannan dambarwa. Shi dai shugaban ƙungiyar ECOWAS kana shugaban Nigeria Alhaji Bola Ahmad Tinubu ya na fuskantar matsin lamba ga majalisar kasar inda ta nuna rashin goyon bayanta da bukatar sa na tura dakaron soja a Nigar. Tuni dai shugaban ƙungiyar kuma shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu, ya ƙaƙabawa sojojin jerin takunkumai, kuma aka yanke masu wutar lantarki da suke samu daga Najeriya, da rufe masu iyakoki wanda hakan ke nufin ba abin da za a shigar a ƙasar, haka su ma ba za su fitar ba. A bangare guda kuma, A Nigeria musamman jihohin arewa maso yamma da suka haɗa da Katsina, Zamfara, Sokoto da sauransu suke  fama da matsanancin rashin tsaro, musamman wani rahoto dake nuna cewa ƙananan hukumomin S...

Shari'ar Musulunci Zata Yi Aiki A Masana'ar Tace Fina-finai Ta Jihar Kano

Image
  Hukumar Tsaftace Fina-Finai Ta Jihar Kano Zata Haɗa Guiwa Da Ma'aikar Addinin Jihar Domin Sanya Ƙafar Wado Ɗaya Ga Masu Karan Tsaye Da Dokokin Hukumar. Sakataren zartarwa na Hukumar Tace Fina-finai na Jihar Kano, Abba El-mustapha ya jaddada aniyarsa ta yin aiki kafada da kafada da ma’aikatar shari’a domin inganta ci gaban hukumar. El-mustapha ya bayyana haka ne ga babban mai shari’a kuma kwamishinan shari’a na jihar Kano Alh Haruna Isah Dederi a jiya yayin wata ziyarar gani da ido da ya kai ma’aikatar

Tsugunni fa bata ƙare ba a Nijar

Image
A sanyin safiyar ranar Lahadi dubun-dubatan al'ummar Nijar ne suka fito zanga-zanga a kofar dandalin Toumo dake birnin Yamai, domin nuna goyon bayansu ga juyin mulkin da sojojin kasar suka yi wanda ya hambarar da shugaba Bazun. Ga wasu hotonan masu zanga zanagar. Bashar Muhammad.